DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za a rika ba mata hutun ‘ta-kaba’ idan mazajensu sun rasu a Katsina

-

Za a rika ba mata hutun ‘ta-kaba’ idan mazajensu sun rasu a Katsina

Google search engine

Gwamnatin jihar ta bullo da sabon tsarin ba mata ma’aikatan da mazajensu suka rasu hutun watanni hudu da kwanaki 10 don su yi ‘ta-kaba’ a jihar.

Musulunci dai ya tanadi ‘ta-kaba’ ga matan da mazajensu suka rasu su zauna gida a killace don jimamin rasuwar mazajen nasu.

Jaridar Punch ta jiyo shugaban ma’aikatan gwamnati a jihar Katsina Falalu Bawale ba cewa an aike da sanarwa ga duk ma’aikatu, sassa da hukumomin gwamnati da su rika ba mata hutun ‘ta-kaba’ idan mazajensu sun rasu.

Hakan dai ya biyo bayan bukatar da majalisar dokokin jihar ta gabatar na neman a samar da tsarin ba da hutun ‘idda’ ga mata ma’aikatan da mazajensu suka rasu, wanda daga bisani sashen zartarwar jihar ya amince.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Sokoto za ta bude kofar tuba ga masu tayar da kayar baya dake neman sulhu a jihar

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana aniyar ta na tattaunawa da masu tada kayar baya da ke dauke da makamai wadanda suke shirye domun ajiye makamansu...

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

Mafi Shahara