DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tarihin siyasar Rabiu Musa Kwankwaso

-

 

Rabi'u Musa Kwankwaso

Babu tantama kai ne jagoran siyasar arewacin Nijeriya kuma jigo a siyasar Nijeriya. Wasu ke nan daga cikin kalaman taya murnar cika shekaru 68 a duniya, da gwamnan jihar Kano Engr Abba Kabir Yusuf ya aike wa mai gidansa Rabi’u Musa Kwankwaso. 

Bikin zagayowar ranar haihuwar Kwankwaso na bana ya zo ne daidai lokacin da gwamnan Kano Abba Kabir ke samun shawara daga wasu ‘yan siyasa na cewa ya daina sauraran shawarwarin mai gidan nasa Kwankwaso karkashin kungiyar Abba Ta Tsaya da Kafarka. Amma gwammnan ya yi watsi da wannan shawara inda ya ce a shekaru 38 da ya yi aiki kafada-kafada, da Kwankwaso ya koyi darussan rayuwa da dama, yana mai siffanta madugun siyasar Kwankwasiyyar a matsayin mutum mai gaskiya da jajircewa wajen samar da ci-gaban al’umma.

To amma ba a taru aka zama daya ba, wadanda ke adawa da tsohon ministan tsaron Nijeriyar na masa kallon dan siyasa mai cike da kura-kurai kamar yadda Musa Iliyasu Kwankwaso ke zargi

Masu sharhi kan al’amuran siyasa a Nijeriya irinsu Dr, Sa’idu Ahmad Dukawa na ganin cewa kamata ya yi a wannan lokacin Engr, Rabiu Musa kwankwaso ya mayar da hankali wajen dawo da tarbiyyar matasa musamman yadda maganarsa ke da tasiri a fagen siyasa.

Tarihin Rabiu Musa Kwankwaso

An haifi tsohon gwamnan Kano Rabiu Musa Kwankwaso ne a ranar 21 ga Oktoban 1956 a garin Madobi dake jihar Kano, Mahaifin sa Alhaji Musa Sale ya rike mukamin dagacin kauyen Kwankwaso daga bisani aka nada shi hakimin Madobi daga masarautar Kano.

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi makarantar firamare a garin Kwankwaso,bayan ya kammala ya wuce Kano Technical College daga nan ya tafi Kaduna Polytechnic inda ya yi karamar Diploma, ya kuma dora da babbar Diploma ta HND. 

Tun daga kwalejin kimiyya da fasaha ta Kaduna,  Kwankwaso, ya kasance shugaban dalibai. Ya yi karatun digirinsa na biyu a Burtaniya daga shekarar 1982 zuwa 1983 a Middlesex Polytechnic da Jami’ar Fasaha ta Loughborough inda ya sami digiri na biyu a fannin injiniya a shekarar 1985. Ya kuma samu shaidar karatun digirin-digirgir  na PhD a Jami’ar Sharda da ke kasar India.

Tsohon sanatan na yankin Kano ta Tsakiya ya fara aiki da hukumar samar da ruwan sha ta Jihar Kano a shekarar 1975. Ya yi aiki na tsawon shekaru goma sha bakwai a wurare daban-daban har ya kai matsayin babban injiniyan ruwa.

A shekarar 1992, Kwankwaso ya zama dan majalisar tarayya zuwa shekarar 1993.

Ya zama gwamnan jihar Kano a karo na farko,a shekarar 1999 zuwa 2003. A 2003 bayan shan kayen zaben gwamna da ya yi yunkurin tazarce ya zama ministan tsaron Nijeriya a lokacin mulkin tsohon shugaban kasa Obasanjo har zuwa 2007.

Sai dai 2011, tsohon gwamnan ya sake fitowa takarar gwamna da karfinsa, inda a tutar jam’iyyar PDP ya samu damar zama gwamnan Kano a karo na biyu har zuwa shekarar 2015.

Daga nan tsohon gwamnan ya zama Sanata a shekarar ta 2015,har zuwa 2019. A shekara ta 2023, Kwankwaso ya yi takarar shugabancin Nijeriya a jam’iyyar NNPP. Duk bai yi nasara ba, ya ci gaba da zama jagora ga a cikin jam’iyyarsa ta NNPP wacce a yanzu haka yake fuskantar takaddamar zargin zama maciji fidda na kogo, inda wadansu da suka yi ikirarin kafa jam’iyyar ke zarginsa da mamaye komai a jam’iyyar. 

DCL Hausa

Sadeeq Muhammad Fagge daga jihar Kano

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara