HomeUncategorizedBa gudu ba ja da baya za muyi zaben kananan hukumomi ranar...

Ba gudu ba ja da baya za muyi zaben kananan hukumomi ranar Asabar-Abba Kabir Yusuf

-

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ce ba gudu ba ja da baya za a gudanar da zabukan kananan hukumomi a ranar Asabar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da yake mika tutocin takara na jam’iyyar  NNPP ga ‘yan takarar shugabanin kananan hukumomin jihar 44 da kansiloli a jihar.

Mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar, ya ce da taron wanda aka gudanar a filin wasa na Sani Abacha a ranar Alhamis ya samu halartar manya-manyan mabiya da magoya bayan jam’iyyar.

A ranar Talata ne wata babbar kotun tarayya karkashin jagorancin mai shari’a Simon Ameboda ta rushe shugabanni da mambobin hukumar zaben jihar KANSIEC tare da dakatar da gudanar da zaben har sai an gyara hukumar yadda ya kamata. 

Gwamnan, ya ce a halin yanzu jihar ba za ta bari wasu suzo su dagula zaman lafiyar da ‘yan kasa ke samu ba, ya kara da cewa gwamnatin jihar da hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar KANSIEC na da dukkan goyon bayan da tsarin mulki ya ba shi wajen gudanar da zaben.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img