DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar Dattawa za ta tantance sabbin ministocin da shugaba Bola Tinubu ya nada

-

 

Majalisar Dattawan Nijeriya

A yau ne majalisar dattawa za ta tantance ministocin da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya mika mata domin tantance su.

Daily Trust ta ruwaito cewa hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta yi bincike tare da wanke wadanda aka nada, gabanin tantance su a yau.

A satin da ya gabata ne dai Tinubu ya yi wa majalisar ministocinsa garambawul, inda ya kori ministoci shida tare da nada wasu sabbi bakwai.

Daily Trust ta ruwaito cewa, a ranar litinin wadanda aka nada sun sun je ofishin mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin majalisar dattawa, Sanata Basheer Lado, domin gabatar da takardunsu.

Sanata Lado, a wata sanarwa da ya fitar, ya tabbatar da cewa, wadanda aka nada a matsayin ministocin, majalisar dattawa, za ta fara tantance su yau a harabar majalisar a Abuja.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara