Jam’iyyun siyasa za su sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya gabanin zaben gwamnan jihar Ondo

-

Farfesa Mahmood Yakubu

Gabanin zaben gwamnan jihar Ondo da za a yi a ranar 16 ga watan Nuwamba, hukumar zabe ta kasa INEC ta bayyana cewa ‘yan takarar da za su fafata a zaben za su rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya wanda kwamitin zaman lafiya na kasa karkashin jagorancin tsohon shugaban kasa Janar Abdulsalami Abubakar yake jagoranta.

Kwamitin na da nufin tabbatar da ‘yan takara sun yi alkawarin gudanar da zabe cikin lumana ba tare da tashin hankali ba.

Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a yayin wani taro da kungiyoyin farar hula.Ya ce kwamitin zaman lafiya na kasa a karkashin jagorancin tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar GFCR, na gudanar da ayyukan sa yadda ya kamata.

Yakubu ya bayyana muhimmancin gudummawar da kungiyoyin farar hula ke da su, inda ya jaddada rawar da suke takawa wajen inganta zabe cikin kwanciyar hankali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara