HomeUncategorizedKungiyar Gwamnonin Nijeriya ta ce tana tausayawa da halin matsi da ake...

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta ce tana tausayawa da halin matsi da ake ciki

-

Kungiyar gwamnonin Nijeriya

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana tausayawa ga ‘yan kasar saboda halin da ake ciki, inda ta amince da kalubalen tattalin arziki da ake fuskanta a Nijeriya, tare da bayyana fatan cewa sauye-sauyen da shugaba Bola Tinubu ya yi zai haifar da sakamako mai kyau nan ba da jimawa ba.

Gwamnan jihar Imo, Sanata Hope Uzodinma, ya bayyana matsayar gwamnonin yayin wata ganawa da manema labarai bayan taron kungiyar NGF a Abuja.

Ya ce cire tallafin man fetur ya kara ta’azzara matsalolin tattalin arziki,tsadar kayayyaki, lamarin da ya sa ‘yan Nijeriya da dama ba sa iya biyan bukatun yau da kullum.

A nasa bangaren gwamnan jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazaq, ya ce kungiyar gwamnonin ta bayyana fatanta na cewa ganawar da suka yi a baya-bayan nan da mukaddashin Darakta Janar na ma’aikatar tsaro  Adeola Ajayi, da kuma ofishin mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro zai karfafa hadin gwiwar tsaro a jihohi.

Ya ce sun kuma gana da Shugaban kamfanin NNPCL, Mele Kyari, wanda ya yi musu bayani kan yadda aka cire tallafin mai gaba daya, kalubalen da kamfanin ke fuskanta, da kuma shirinsa na rage radadin radadin da suke fuskanta na hauhawar farashin litar mai na baya-bayan nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img