DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ganduje na jagorancin APC da kyau da kwarewa – ‘Yan Arewa ta tsakiyar Nijeriya

-

Gamayyar kungiyoyin jami’iyyar APC na yankin Arewa ta tsakiyar Nijeriya ta yi jinjina ga salon jagorancin Shugaban jami’iyyar APC na kasa na Abdullahi Umar Ganduje.
Kungiyar ta ce Ganduje na nuna kwarewa wajen tafiyar da jami’iyyar a matakin kasa musamman ganin yadda ya kwamitin yakin neman zaben Gwamnan jihar Ondo mai zuwa.
Shugaban kungiyar a wani taron manema labarai a Jos babban birnin jihar Plateau, Hon Saleh Abdullahi Zazzaga ya ce abin a yaba ne ganin yadda Ganduje da sauran shugabancin APC ya jawo wasu ‘ya’yan kungiyar da ma karin wasu bangarori domin tafiya tare da su a harkokin jami’iyyar.
A ranar 28 ga watan Oktoba, Abdullahi Ganduje ya kafa kwamitin mutane 305 da za su ba da gudunmuwa don tunkarar zaben Gwamnan jihar Ondo. Gwamnan jihar Lagos Babajide Sanwo-Olu me ke jagorantar kwamitin. Kazalika, Gwamnan Ogun Dapo Abiodun ne shugaban kwamitin kula da harkokin kudi, yayin da Sanata Godswill Akpabio ne mataimakinsa.
Bugu da kari, akwai Gwamnan jihar Yobe Mai Mala Buni da Ministan yada labarai Mohammed Idris a matsayin Shugaba da mataimakinsa a kwamitin yada labarai. 
Saleh Abdullahi Zazzaga ya ce wannan ya nuna karara yadda Abdullahi Ganduje ya himmatu wajen ganin an hada kan ‘ya’yan Jami’iyyar a mataki daban-daban.
Ya ma bukaci Ganduje da ya cigaba da tafiya da kowa da kowa domin ba kowa damar ba da tashi gudunmuwa don jami’iyyar ta cigaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara