DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu zai rantsar da sabbin ministocinsa 7 a ranar Litinin

-

 

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu zai rantsar da sabbin ministocinsa guda 7 da ya nada a makon jiya

Bayanin hakan na kunshe a cikin wata sanarwa da Bayo Onanuga mai magana da yawun shugaban na Nijeriya ya fitar a ranar Lahadi 

Ministocin da za a rantsar sun hada da;

1. Bianca Odinaka Odumegu-Ojukwu wacce aka naɗa ta ministar ƙasa a ma’aikatar harkokin waje.

 

2. Jumoke Oduwole matsayin ministar masana’antu da kasuwanci da zuba jari.

3. Dr Nentawe Yilwatda ministar jin ƙai.

4. Muhammadu Maigari Dingyadi matsayin ministan ƙwadago da samar da ayyukan yi.

5. Idi Mukhtar Maiha ministan ma’aikatar kiwo.

6. Yusuf Abdullahi Ata matsayin ƙaramin ministan gidaje da ci gaban birane.

7. Dr Suwaiba Sa’id Ahmad da ta zama sabuwar ministar ilimi.

A ranar 23 ga watan Oktoba ne dai shugaban na Nijeriya ya sanar da korar ministoci 5 daga gwamnatinsa bisa laakari da rashin kwazon su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara