HomeUncategorizedSufeton 'yan sandan Nijeriya ya ba da umarnin bincike kan cin zarafin...

Sufeton ‘yan sandan Nijeriya ya ba da umarnin bincike kan cin zarafin yaran da aka kama yayin zanga-zangar#BadGovernance

-

Kayode Egbetokun

Babban Sufeton ‘yan sandan Nijeriya Kayode Egbetokun, ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan zarge-zargen cin zarafin kananan yara da aka kama yayin zanga-zangar #BadGovernance

 Jaridar PUNCH  ta rawaito cewa a ranar Juma’a, an gurfanar da mutane 76 da ake zargi, galibinsu kananan yara da ba su samu isasshen abinci mai gina jiki ba,shida daga cikin yara kanana sun fadi a wajen shari’ar hakan yasa aka a fitar da su daga wurin shari’a domin samun agajin gaggawa.

Da yake mayar da martani game da lamarin a ranar Asabar, IG ya yi iƙirarin cewa suman da wasu yara ƙanana sukai a kotun an shirya shi ne don jawo hankulan mutane.

Bayan da al’umma suka nuna bacin ransu kan lamarin, shugaban kasa Bola Tinubu ya bayar da umarnin a janye tuhumar da ake yi wa kananan yaran.                    

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan Muyiwa Adejobi ya fitar a daren ranar Litinin, ya bayyana cewa IG ya bayar da umarnin gudanar da bincike yaran a lokacin da suke tsare.

 Adejobi ya kara da cewa, da samun rahoton binciken, IG ya sha alwashin magance duk wasu kura-kurai da aka gano.

 Ya ce babban sufeton ‘yan sandan , yayin da yake birnin Algiers na kasar Aljeriya don halartar taron kwamitin hadin gwiwar ‘yan sanda na kungiyar Tarayyar Afirka, ya ba da umarnin gudanar da bincike kan lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img