DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Jihar Kano ya roki kungiyar likitoci ta kasa reshen jihar da su janye daga yajin aiki da suka tsunduma yi

-

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya yi kira ga kungiyar likitoci ta Nijeriya reshen jihar da ta dakatar da yajin aikin da ta ke yi domin kaucewa jefa rayukan al’ummar Kano sama da miliyan 20 cikin hadari.

Daily Trust ta ruwaito cewa Gwamna Yusuf ya kafa wani kwamiti domin bincike kan zargin cin zarafin da kwamishiniyar jin kai ta jihar, Amina Abdullahi HOD,ta yi wa wata likita a ranar Litinin a asibitin kwararru na Murtala Muhammed da ke Kano.

Kungiyar likitocin ta bai wa gwamnatin jihar wa’adin awanni 48 da ta kori kwamishinan jin kai, kuma ta sha alwashin ci gaba da yajin aiki , idan har gwamnati ta gaza biya mata bukatar ta.

Sai dai gwamnan da ya ke mayar da martani kan lamarin a yayin wani taron manema labarai da akai kai tsaye a gidan gwamnatin jihar ya bayyana rashin jin dadin sa kan matakin da kungiyar ta dauka bayan wata rashin fahimta juna da aka samu tsakanin tsakanin su.

Gwamnan ya jaddada cewa kungiyar za ta iya baiwa kwamitin binciken damar gudanar da bincike kan lamarin tare da daukar kwakkwaran mataki, maimakon dai na ayyukan su hakan zai taba wa’yanda basu ji ba basu gani ba a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara