HomeUncategorizedMasu hakar ma'adinai 22 ne suka rasa rayukansu sakamakon ruftowar kasa a...

Masu hakar ma’adinai 22 ne suka rasa rayukansu sakamakon ruftowar kasa a jihohin Adamawa da Taraba

-

Masu hakar zinare

Akalla ma’aikatan hakar ma’adinai 22 ne ake kyautata zaton sun rasa rayukansu sakamakon ruftowar kasa da ake hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, wanda ke cikin wani gandun daji na kasa da ya kai karamar hukumar Gashaka a jihar Taraba da kuma karamar hukumar Toungo a jihar Adamawa.

Adamu Jamtare, wani mai hakar ma’adinai daga Gashaka, ya bayyana cewa da yawa daga cikin wadanda suka rasu sun fito ne daga garin Jamtare da ke karamar hukumar Gashaka ta jihar Taraba.

Ya ce suna hakar zinare ne a wani yanki da ake kira Buffa zone a cikin wani gandun dajin Gashaka-Gumti, wanda tsayin sa ya mamaye sassan Gashaka da Toungo kuma dukkan masu hakar ma’adinai 22 da suka makale a cikin ramin ana kyautata zaton sun mutu.

Shugaban karamar hukumar Toungo ta jihar Adamawa, Injiniya Suleiman Toungo, ya tabbatar da cewa an gano gawarwakin masu hakar ma’adanai 5,duk da cewa bai da tabbas kan adadin wadanda ke cikin ramin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img