DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dan wasan gaba na Najeriya Ademola Lookman, ya shiga jerin wadanda aka zaba domin karbar kambun gwarzon dan wasan kwallon kafa na duniya na shekara ta 2024.

-

Dan wasan Najeriya Ademola Lookman ya shiga cikin jerin fitattun yan  wasan kwallon kafa da su ka hada da Lionel Messi, da Cristiano Ronaldo, da Kylian Mbappé, da kuma Erling Haaland, wadanda aka zaba domin karbar kyautar gwarzon dan wasan kwallon kafa na shekara ta 2024.

Wannan dai wani bangare ne na bukukuwan bada lambar yabo na shekara-shekara na Globe Soccer wanda Hukumar Wasannin Dubai ke shiryawa.

Sanarwar da Globe Soccer Awards su ka wallafa a shafin X a wannan Alhamis, ta ce dan wasan Najeriya Ademola Lookman na cikin wadanda aka zabo domin cin kyautar gwarzon dan wasan kwallon kafa na duniya na 2024.
 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara