DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC ta lashe zaben Gwamnan jihar Ondo

-

Hukumar zabe a Nijeriya ta bayyana gwamna Lucky Aiyedatiwa a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Ondo da kuri’u 366,781.

Shi kuwa ‘dan takarar jami’iyyar PDP kuma tsohon mataimakin gwamna Agboola Ajayi ya samu kuri’u 117,845.
Jam’iyyar Labour Party da ta samu kuri’u 1,162 kamar yadda RFI Hausa ta rawaito.
Shugaban jami’ar gwamnatin tarayya dake Lokoja kuma baturen zaben Farfesa Olayemi Akinwunmi ne ya gabatar da sakamakon zaben a gaban ‘yan jarida bayan kammala tattara alkaluman kananan hukumomi 18 wadanda aka tabbatar da nasarar Aiyedatuwa a cikin su baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara