Cutar kwalara ta yi ajalin mutane 25 a Sokoto, yayin da 15 ke kwance a asibiti

-

 

Cutar kwalara ta yi ajalin  mutane 25 a Sokoto, yayin da 15 ke kwance a asibiti

Akalla mutum 25 ne aka tabbatar da mutuwar su daga cikin  mutane 1,160 da su ka kamu da cutar Kwalara a jihar Sokoto. 

Kwamishiniyar lafiya ta jihar Asabe Balarabe, ta bayyana haka a ranar Litinin a lokacin da take zantawa da manema labarai.

Majiyar DCL Hausa wato Jaridar Punch, ta ambato kwamishiyiyar na cewa zuwa yanzu mutum 15 a ke ci gaba da kulawa da su a asibiti, a kananan hukumomin Sokoto ta Arewa da Silame da kuma Kware.

Yayinda gwamnatin jihar ke ci gaba da kokarin dakile yaduwar cutar, a cewar Hajiya Asabe Balarabe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara