HomeUncategorizedGwamnan Jihar Kebbi ya ba da umurnin kamo wasu mutane da ake...

Gwamnan Jihar Kebbi ya ba da umurnin kamo wasu mutane da ake zargi da hannu wajen kai hari ga fulani

-

 

Gwamnan Kebbi Nasir Idris

Gwamnan jihar Kebbi Nasir Idris ya ba da umurnin kama wasu mutane da ake zargi suna da hannu a harin da aka kai wa wasu fulani biyo bayan harin da kungiyar Lakurawa ta kai Mera

A wata ziyarar jaje da ya kai garin Mera dake karamar hukumar Augie, gwamnan yayi Allah wadai da harin ramuwar gayya wanda yayi sanadiyar halaka wasu Fulani guda shida.

Rahotanni sun nuna cewa an kai harin ne kan Fulanin da ake zargin suna da hannu a harin Mera na farko, inda ‘yan ta’addan Lakurawa suka kashe mutane 17. 

Da yake jawabi ga mazauna yankin da lamarin ya faru Gwamnan ya nuna damuwar sa bisa faruwar lamarin, inda ya ce, ya bayar da umarnin a kamo wadanda ke da hannu wajen harin da aka kai wada Fulanin da ba su ji ba ba su gani ba da sunan ramuwar gayya.

            

Gwamnan ya jaddada cewa bai kamata mutane su dunga daukar doka a hannunsu ba, ya kuma bukace su da sukai rahoto ga jami’an tsaro da zarar suka ga wani abu da basu amince da shi ba

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img