Gwamnatin Nijeriya ta ware Naira biliyan 112 don tabbatar da tsaro da kulawa a makarantun yara cikin shekaru uku masu zuwa

-

Shugaba Tinubu

Ministar harkokin mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba a Abuja domin tunawa da ranar yara ta duniya.

Ana bikin ranar yara a kowace shekara a duniya a ranar 20 ga Nuwamba, kuma rana ce da majalisar dunkin duniya ta ware domin ‘yancin yara. 

Sakamakon haka, majalisar dinkin duniya ta yi bikin a wannan rana tare da kokarin wayar da kan al’umma game da muhimmancin ilimin yara, kula da lafiyar su da kuma bukatar magance matsalolin da yaran ke fuskanta.

Ministar harkokin mata, don haka ta ce gwamnati ta himmatu wajen samar da yanayin da kowane yaro zai samu ilimi da lafiya da rayuwa ingantacciya ba tare da tsoro ko cutarwa ba.

A cewarta, an ba da tallafin ne ta hanyar sabon tsarin kula da makarantun yara tare da bayar da tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara