DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya rubuta wa majalisa, yana neman ta amince da nadin Janar Oluyede a matsayin babban hafsan sojin kasa na Nijeriya

-

A cikin wasikar da ya rubuta wa shugaban majalisar Dattawa Sanata Godswill Akpabio da kakakin majalisar wakilai Hon Tajuddeen Abbas, Shugaba Tinubu ya bukaci majalisun sun tabbatar da nadin bisa la’akari da tanadin doka a sashe na 218(2) na kundin tsarin mulkin Nijeriya da aka yi wa gyara a 1999 da kuma sashe na 18(1) na dokar da ta kafa rundunar soji.
Shugaba Tinubu dai ya nada Janar Oluyede a matsayin mukaddashin babban hafsan sojin kasa na Nijeriya a ranar 30 ga watan Oktoba, 2024 bayan jinya da Janar Lagbaja ya tafi, ba a ma jima ba, Janar Lagbaja ya rasu a ranar 5 ga watan Nuwamba.
Kafin nadin nasa, Janar Oluyede shi ne kwamandan rundunar sojin kundumbala da ke Jani, jihar Kaduna.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara