DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za a dakatar da daliban da ke tsangwamar abokan karatunsu – Gwamnatin Nijeriya

-

Ma’aikatar ilimi ta tarayya ta yi gargadin cewa duk dalibin da aka samu da laifin cin zarafin da ya kai ga taba lafiyar abokan karatunsu, za a dakatar da shi daga kwalejojin tarayya har sai yadda hali yayi.
Wata takardar umurni da babban sakataren ma’aikatar, Nasir Gwarzo, ya sanyawa hannu ta ce ba za su zuba ido dalibai na raunata junansu ba a cikin makarantu.
Sanarwar ta ce ko a ranar 7 ga watan Nuwamba, gwamnatin tarayya ta bada umurnin dakatar da wasu dalibai 13 na tsawon makonni 6 a jihar Enugu har sai an gudanar da bincike kan zargin da ake musu na tsangwamar abokan karatunsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara