DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wasu mahara sun sace mutum hudu ‘yan gida daya a jihar Kaduna

-

 

Al’ummar yankin Keke A dake rukunin gidajen Kaduna Millennium City sun shiga firgici, bayan sace wani yaro dan shekaru biyu tare da ‘yan uwansa mata uku da wasu ‘yan ta’adda suka yi.
An ruwaito cewa, matan wadanda aka sace ‘yan shekaru 9, da 12, da kuma 15 ne, kuma daya daga cikinsu marainiya ce. kamar yadda mahaifin yaran Yunusa Sarkin Samarin Keke ya shaidawa jaridar Dailytrust.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 9 na daren Talata, lokacin da mahaifin yaran ya tafi asibiti domin duba mahaifiyar yaran wadda ke kwance a asibiti.
Duk kokarin jin ta bakin kakakin ‘yan sandan jihar Kaduna ASP Mansur Hassan hakan ya ci tura, kuma bai mayar da sakon waya da aka tura masa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara