DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta ba da tallafin kudi ga masu kananan kasuwanci a jihar Ebonyi

-

 

Bankin masana’antu BOI, ya ce akalla ‘yan kasuwa sama da 14,776 ne daga jihar Ebonyi suka ci gajiyar shirin ba da tallafin da gwamnatin tarayya ta kaddamar  a jihar.

Chukwudi Asiegbu, manajan BOI a Ebonyi ne ya bayyana hakan a yayin wani taron majalisar gari kan sakamakon shirin bayar da tallafin a ranar Juma’a a Abakaliki.

Asiegbu ya ce kowane dan kasuwa daga cikin wadanda suka ci gajiyar shirin an ba shi Naira 50,000 wanda jimilla kudin sun kai Naira miliyan 738.8.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara