HomeUncategorizedBa na jayayya da Shugaba Tinubu, kira kawai nake da a kara...

Ba na jayayya da Shugaba Tinubu, kira kawai nake da a kara yin tuntuba kan dokar haraji – Gwamna Zulum

-

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya yi kira da a kara duba na tsanaki kan kudirin sake fasalin haraji da majalisar dokokin Najeriya ke nazari a kai, inda ya ce ba ya adawa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu. 
Zulum ya bayyana haka ne ta cikin wani shirin siyasa na gidan Talabijin na Channels, inda ya jaddada muhimmancin hada hannu da masu ruwa da tsaki don magance dukkan matsalolin da ke tattare da kudirin. 
A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai Dauda Iliya, ya fitar a Litinin din nan, Gwamna Zulum ya ce “tuntuba, babbar jigo ce ga al’ummar da ta rungumi tafarkin dimokuradiyya.”
Gwamnan ya nuna damuwarsa, tare da yin gargadin cewa wannan kuduri zai amfanar da jihohi kamar Lagos da Rivers ne kawai, abin da zai iya jefa sauran jihohin cikin mawuyacin hali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img