DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kashi 70 cikin 100 na ‘yan Najeriya sun ƙi karbar tayin karbar cin hanci a shekarar 2023 – ICPC

-

Shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta ta Nijeriya ICPC, Musa Adamu Aliyu (SAN) ya ce Kashi 70 cikin 100 na ‘yan Nijeriya da aka yi wa tayin karbar cin hanci a shekarar 2023 sun ƙi karba.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da hukumar ke neman hadin haɗin kan sauran hukumomi wajen yaki da cin hanci da rashawa, ganin cewa babu wata hukuma guda da za ta iya wannan aiki ita kadai. 
Shugaban hukumar ta ICPC ya bayyana hakan ne yayin wani taro da ya gudana a jihar Kano kan karfafa aikin hukumar na dakile cin hanci da rashawa. 
Taron wanda babbar manufarsa ita ce samar da hadin gwiwa wajen yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya. 
Ya ce, babu wani bangare na gwamnati ko matakin gwamnati ko hukuma da zai iya yaki da cin hanci da rashawa don haka akwai bukatar samun hadin kai don ganin an kai ga gaci.
Yayin taron babbar Jojin jihar Kano, Mai Shari’a Dije Abdu Aboki, ta yaba da yadda hukumar ta ICPC ke bibiyar matakan da suka dace wajen yaki da cin hanci da rashawa. 
Ta ce aiwatar da doka da kuma gurfanar da wadanda ake zargi wajibi ne, amma yin kan da garki dabara ce, wadda ke magance tushen cin hanci da rashawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara