DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta yi watsi da bukatar bada belin tsohon gwamnan Kogi Yahaya Bello

-

Yahaya Bello

Babbar kotun tarayya da ke Maitama a babban birnin Nijeriya Abuja, ta yi watsi da bukatar bayar da belin tsohon Gwamnan Jihar Kogi Yahaya Bello. 

Da ta ke yanke hukunci a zaman kotun na ranar Talata mai shari’a Maryanne Anenih, ta yi zargin rashin cancantar neman belin na Yahaya Bello.

Tun da farko, hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta Nijeriya EFCC ce, ta gurfanar da Yahaya Bello, tare da wasu mutane biyu a gaban kotun, bisa tuhumar su da karkatar da makudan kudade da yawansu ya kai Naira biliyan 110.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara