DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za a kara adadin lantarkin da ake samarwa nan da watan Janairu – Ministan lantarki

-

Ministan lantarki, Adebayo Adelabu, ya ce ana ci gaba da shirye-shiryen samar da karin megawatts 150 na wutar lantarki a Nijeriya nan da watan Janairun 2025.

Ministan ya bayyana haka ne a fadar shugaban kasa ranar Laraba, inda ya ce matakin zai magance matsalolin da ake fuskanta na katsewar manyan tashoshin lantarki a fadin kasar.

Adelabu, wanda ke cikin ganawar da aka yi tsakanin shugaba Bola Ahmed Tinubu da takwaransa na Jamus, Frank Walter Steinmeier, ya ce hanyar da za a bi wajen tabbatar da samar da wutar lantarki shi ne hadin gwiwa, da kuma sabunta manyan tashoshin samar da lantarki. 

Ya ce tuntuni Nijeriya da Jamus suna da dadaddiyar alaka a fannin makamashi da wutar lantarki, saboda akwai bukatar sabunta wannan alaka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara