HomeUncategorizedGwamnonin Nijeriya sun goyi bayan kafa ‘yan sandan jihohi

Gwamnonin Nijeriya sun goyi bayan kafa ‘yan sandan jihohi

-

Gwamnonin Nijeriya 

Gwamna jihar Kaduna Uba Sani, ya ce jihohi 36 na Nijeriya sun amince da kafa ‘yan sandan jihohi, bayan mika rahotonsu ga majalisar tattalin arzikin kasa.

Gwamnan ya bayyana haka ne a zantawarsa da manema labarai, jim kadan bayan kammala taron majalisar tattalin arzikin kasa karo na 147 wanda mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya jagoranta a Abuja.

Uba Sani ya bayyana cewa jihohi da dama sun amince da kudurin kafa ‘yan sandan jihohi duba da yadda kusan kowace jiha ke fama da kalubalen tsaro. 

Ya kara da cewa hukumomin tsaron da ake da su, ba su da isassun jami’an da za su yi aiki a duka jihohin da kuma kasa baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img