DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar ECOWAS ta matsa kaimi domin samar da kudin bai daya ga mambobin ta

-

 

Kungiyar ECOWAS ta matsa kaimi domin samar da kudin bai daya ga mambobin ta

Kungiyar ci gaban kasashen yammacin Afrika ECOWAS ko kuma CEDEAO, na ci gaba shirye-shirye kaddamar da kudin bai daya a yankin mai suna ECO, biyo bayan cimma matsayar da aka yi a yayin taron kasashen karo na 65.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwar karshen taron da shugabannin  kasashen suka gudanar karo na 66 a tarayyar Nijeriya Abuja.

A baya dai kungiyar ECOWAS dake da kasashe 15, ta shirya kaddamar da kudin ECK a shekarar 2020, amma cutar korona ta kawo tsaiko inda a halin yanzu aka sanya 2027 a matsayin ranar kaddamarwa.

Hukumar ta ce ta yi amfani da shawararin da babban kwamiti ya gabatar, na zabar kasashe da za a kaddamar da tsarin da kuma wadanda za su shigo daga baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna kokarin bunkasa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan 1 – Kashim Shettima

Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya ce gwamnatin kasar na kan hanyar bunkasa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan 1 cikin shekaru goma masu zuwa. Kashim...

Yan sanda sun dakile yunkurin garkuwa da direba da fasinjoji a Katsina

Jami’an rundunar ‘yan sandan Nijeriya sun dakile wani yunkurin yin garkuwa da mutane a hanyar Funtua zuwa Gusau a Katsina. Jami’an sun yi artabu da ‘yan...

Mafi Shahara