DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta ci tarar kudi Naira milyan 3 ga hukumar lura da shige da fice ta Nijeriya

-

Fasfo

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta umarci hukumar kula da shige da fice ta Nijeriya NIS da ta biya Benita Ezumezu diyyar Naira miliyan 3 sakamakon gaza ba ta fasfo din ta cikin makonni shida da aka kayyade. 

Kotun ta kuma umarci Olubunmi Tunji-Ojo, ministan harkokin cikin gida, da hukumar ta NIS, su tabbatar da cewa wadanda suka cika dukkan sharudda an basu fasfon su cikin makonni shida kamar yadda doka ta 9(4) ta dokar hukumar shige da fice ta shekarar 2015 ta tanada. 

Alkalin kotun, Mai shari’a Emeka Nwite, ya bayar da umarnin ne a lokacin da yake yanke hukunci a wata kara mai lamba FHC/ABJ/CS/75 da Benita Ezumezu ta shigar, sakamakon bata ma ta lokaci da aka yi har tsawon wasu watanni kafin ta samu fasfo dinta, wanda ta nema a watan Oktoban 2022.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara