DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Zamfara ta nemi agajin tarayya, bayan Bello Turji ya yi barazanar kaddamar da hare-hare a wasu yankunan jihar

-

Gwamnatin jihar Zamfara ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta dauki mataki kan kasurgumin dan bindiga Bello Turji, bayan da ya yi barazanar kai hare-hare kan al’ummomin Zamfara da Sokoto.
A cikin wani bidiyo da ya fitar a ranar Laraba, Turji ya ce idan har jami’an tsaro ba su saki makusancinsa Bello Wurgi da aka kama ba to zai hana zaman lafiya a yankin.
Da yake mayarda martani kan barazanar, mai baiwa gwamnan jihar Zamfara shawara kan hulda tsakanin hukumomin gwamnati Dr Sani Shinkafi ya yi kira ga Shugaban Bola Ahmad Tinubu da ya dauki matakin gaggawa kan wannan batu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara