DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya za ta kashe Naira biliyan 60 wajen ciyar da daliban Firamare abinci mai gina jiki cikin kasafin kudin shekarar 2025

-

 

Gwamnatin Nijeriya ta ware Naira biliyan 60 cikin kasafin kudin shekarar 2025 don ciyar da makarantun firamare abinci mai gina jiki a matsayin daya daga cikin sabbin tsare tsare da ma’aikatar ilimi ta kasar za ta aiwatar.

Idan dai za a iya tunawa tsohon ministan ilimi na kasar ya bayyana cewa ma’aikatar za ta gudanar da shirin ciyar da makarantu abinci mai gina jiki,kafin shugaban kasar ya tsige shi.

Sai dai an ware Naira biliyan 50 cikin kasafin kudin na shekarar 2025,domin tallafa wa shirin maido da yaran da ba sa zuwa makaranta, tare samar da kayayyakin koyo da koyarwa na zamani ga makarantun firamare da sakandare a cikin jihohi 36 da ke kasar kamar yadda Daily Trust ta rawaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara