DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dan wasan Najeriya Sadiq Umar ya kammala komawa kungiyar Valencia

-

Dan wasan gaba na tawagar kwallon kafa ta Real Sociedad dake buga gasar La liga ta kasar Spain , Sadiq Umar ya kammala komawa tawagar Valencia CF dake kasar ta Spain a matsayin aro na wata shida.
Mai shekaru 26, dan wasan dan asalin jihar Kaduna kuma dan wasan gaba na tawagar Najeriya wato Super Eagles, ya koma ne bayan cimma yarjeniya da Valencia, a yayin da aka bude kasuwar musayar ‘yan wasa a watan Janairu.
Sadiq zai yi amfani da riga mai lamba 12 a tawagar ta Valencia, abinda hakan ke zama wani sabon shafi ga dan wasan da yayi fama da jinyar raunin da ya samu a kakar shekarar bara ta 2023/24, wanda ya hana shi buga gasar kofin Afirka na AFCON, da Najeriya ta zo a mataki na biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara