DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda sun kubutar da mutum 18 da aka sace kan hanyar Funtua-Gusau

-

Akalla mutane 18 ne rundunar ‘yan sandan jihar Katsina suka ceto a hannun ‘yan bindiga bayan dakile wani yunkurin garkuwa da mutane a kan hanyar Funtua-Gusau da ke jihar Zamfara.
Rundunar tace ta kuma yi nasarar kwato wasu dabbobi da aka yi yunkurin sacewa a kauyen Gidan Gada dake karamar hukumar Kafur ta jihar Katsina.
Da yake jinjinawa jami’an ‘yan sanda kan wannan kokarin, kwamishinan ‘yan sandan jihar CP Aliyu Abubakar Musa, ya bukaci al’umma su ci gaba da goyon bayan jami’an tsaro tare da kwarmata musu bayanai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara