DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Faransa bata da ikon juya kasashen Afirka – Firaministan Senegal, Ousmane Sanko

-

Ousmane Sanko

Firaministan kasar Senegal Ousmane Sanko, ya caccaki shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron, bisa kalaman sa na cewar kasar na bada kariya ga kasashen Afirka.
Wannan dai na a cikin wani sako da Firaministan ya wallafa a shafin sa na Facebook, Ousmane Sanko ya caccaki kasar Faransa da kawo rikice-rikice da dama maimakon cigaban a nahiyar.
Ya kuma zargi Faransa da waragaza kasar Libya wanda hakan ya haddasa tabarbarewar kalubalen tsaro a yankin Sahel.
A baya bayan an alakanta koma bayan karfin ikon da Faransa ke dashi a yankin yammacin Afirka bisa rashin adalci da kulla kakkarfar alaka da kasar Rasha.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara