DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba da gan-gan harin da muke kai wa ‘yan ta’adda ke shafuwar fararen hula ba – Sojojin Nijeriya

-

 Ba da gan-gan harin da muke kai wa ‘yan ta’adda ke shafuwar fararen hula ba – Sojojin Nijeriya

Rundunar sojin Najeriya ta ce duk hare-hare ta sama da take kai wa ga masu aikata laifukan ne ba fararen hula ba.

Babban Hafsan Sojojin Najeriya Janar Christopher Musa ne ya bayyana haka a wata hira da yayi a gidan Talabiji na Arise TV, a lokacin da yake mayar da martani game da mutuwar fararen hula sama da 10 sanadiyar harin da sojojin suka kai kwanan nan a Zamfara.

Janar Christopher Musa, wanda ya bayyana cewa sojoji sun bi ka’idoji masu tsauri kafin aiwatar da duk wani hari ta sama, ya jaddada cewa sojojin na kai hare-hare ta sama daidai gwargwado domin kawar da yan ta’adda dake addabar wasu sassan jihohin Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara