DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Iyalan waɗanda harin jirgin sama ya rutsa da su a jihar Zamfara sun nemi a biya su diyya

-

Iyalan wadanda harin jirgin saman Sojin Najeriya ya yi ajalin su bisa kuskure a kananan hukumomi Zurmi da Maradun a jihar Zamfara sun nemi gwamnati ta biya su diyya.

Harin wanda jirgin ya kai na ranar 11 ga Janairu 2024 a kauyen Gidan Kara da Malikawa sai Sakida tare da Kakidawa da Tungar Labbo dake Gidan Goga a kananan hukumomin na Zurmi da Maradun, ya yi sanadiyyar rayukan mutum 15 da raunata 9.
Kawo yanzu wadan da suka samu rauni na cigaba da karbar kulawar likitoci a Asibitin Kaura -Namoda dake jihar.
Daya daga cikin iyalan wanda suka nemi biyan diyyar Muhammad Aminu, a zantawar sa Jaridar Daily Trust ta wayar Tarho , ya ce suna kira ga gwamnatin jihar Zamfara da ta Najeriya da su gaggauta biyan su diyya sakamakon halin da aka jefa su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara