DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya yi jinjina ga Gwamnonin Nijeriya da suka goyi bayan kudirin garambawul ga dokar haraji

-

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yabawa gwamnonin jihohin kasar bayan da suka amince da kudirin garambawul na dokar haraji, dake gaban Majalisu.

Shugaban ya kuma ya yabawa shugaban kungiyar gwamnonin gwamnan jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazaq bisa hade kan gwamnonin da yayi suka aminta da lamarin na haraji.
Ta cikin sanarwar da jami’in yada labaran sa Bayo Onanuga ya fitar, Tinubu ya ce gyara fare da yin kwaskwarima ga tsohon tsarin karbar haraji na da matukar muhimmanci.
A karshe ya bukaci Majalisar dokoki da su yi hanzarin sahale kudirin domin ya zama doka da al’ummar Najeriya za su amfana da shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara