DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mutane 86 suka mutu sanadiyar fashewar motar man fetur jihar Neja, an binne 80 a kabari daya – Hukumar NSEMA

-

Biyo bayan fashewar motar man fetur a mararrabar Dikko Junction, dake karamar hukumar Gurara jihar Niger, hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar NSEMA ta ce zuwa yanzu mutum 86 suka mutu.
Wani bayani da daraktan yada labarai na hukumar Abdullahi Baba-Arah ya fitar, ya ce hukumar ta tattara gawarwakin mutanen ne tare da taimakon jami’an karamar hukumar Gurara da kuma jami’an sa kai.
Daga cikin wadanda suka mutu an binne mutum 80 a kabari daya a cibiyar kafiya ta Dikko yayinda biyar aka hannunta su ga ‘yan uwansu, mutum daya kuma ya mutu daga baya saboda raunin da ya ji.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara