HomeUncategorizedMahajjata daga Nijeriya za su biya Naira milyan 8.4 kudin aikin hajji...

Mahajjata daga Nijeriya za su biya Naira milyan 8.4 kudin aikin hajji a shekarar 2025

-

 

Hakan na kunshe a cikin wata sanarwa da mataimakiyar daraktan yada labaran hukumar Fatima Sanda Usara ta fitar a ranar Litinin. 

Sanarwar ta ce hukumar karkashin jagorancin shugabanta Farfesa Abdullahi Sale Usman tare da manyan sakatarorinta da masu ruwa da tsaki sun cimma matsaya bisa duba na tsanaki kan kudin da kowane Alhajin Nijeriya zai biya a shekarar 2025.

A cewar sanarwar mahajjatan da suka fito daga shiyyar Borno da Adamawa,za su biya Naira miliyan 8.3.Hakazalika, maniyyatan da suka fito daga jihohin Kudu za su biya Naira miliyan 8.7.

Sai kuma alhazan da suka fito daga yankin Arewa za su biya Naira miliyan 8.4.

Shugaban hukumar Farfesa Saleh ya bukaci mahajjatan da suke son zuwa aikin Hajji da su bi dukkan ka’idojin kasar Saudiyya ta gindaya tare da jaddada muhimmancin biyan kudi da wuri da kuma yin rajista a kan lokaci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img