Rikakkun ‘yan bindiga biyu sun mika wuya tare da makamansu a jihar Katsina

-

 

Malam Dikko Umaru Radda

Wasu rikakkun ‘yan bindiga guda biyu a jihar Katsina sun mika wuya tare da makamansu da wasu mutane sama da 15 da suka yi garkuwa da su a karamar hukumar Batsari da ke jihar.

‘Yan bindigar da suka mika wuyan sun hada da Abu Radde da Umar Black.

An alakanta mika wuyan nasu da zafafan hare-haren da sojojin hadin gwiwa na Operation fansar yamma da sauran jami’an tsaro ke cigaba da gudanarwa a yankin.

Wasu majiyoyi sun shaidawa gidan talabijin na Channels a ranar Litinin cewa bikin mika wuya da aka gudanar a ranar Lahadi ya samu halartar manyan masu ruwa da tsaki da suka hada da wasu wakilai daga sojoji da shugabannin gargajiya da na addini a yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara