DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu zai bar Abuja a ranar Lahadi zuwa kasar Tanzaniya, domin halartar taron shugabannin kasashen Afirka

-

 

Shugaba Tinubu

Mataimaki na musamman ga shugaban kasar kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar.

Taron wanda gwamnatin Tanzaniya ta shirya tare da hadin gwiwar bankin raya Afirka da bankin duniya, zai mayar da hankali kan shirin samar da wutar lantarki ga mutane miliyan 300 a Afirka nan da shekarar 2030.

A yayin taron shugabannin kasashen Afirka da shugabannin kamfanoni masu zaman kansu, kungiyoyin farar hula, za su tsara dabarun kara samar da makamashi a Nahiyar Afirka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara