DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaban jam’iyyar APC a Nijeriya Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya karbi ‘yan jam’iyyun PDP, NNPP, PRP, da suka sauya sheka zuwa APC a jihar Katsina

-

 

Dikko Umar Radda/Abdullahi Umar Ganduje

Wadanda suka sauya shekar yawancin sun fito ne daga jam’iyyar PDP, NNPP, Accord Party, da Jam’iyyar PRP.

Guda daga cikin wadanda suka sauya shekar shi ne dan takarar mataimakin gwamnan jihar Katsina a jam’iyyar PDP a zaben 2015 Rabiu Bakori.

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje tare da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na kasa ne suka karbi wadanda suka sauya sheka a yayin kaddamar da yakin neman zaben kananan hukumomin jam’iyyar APC da aka gudanar a karamar hukumar Ingawa a ranar Lahadi.

Ganduje, ya bayyana ranar a matsayin rana mai girma da tarihi a jihar Katsina, ya kuma ba da tabbacin cewa za a yi wa wadanda suka sauya sheka adalci.

 Ya ce jam’iyyar APC ita ce kadai jam’iyyar da ta cancanci shiga da ke yin abin da ya dace ta hanyar isar da ribar dimokuradiyya ga ‘yan kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara