DCL Hausa Radio
Kaitsaye

AFCON 2025: CAF ta sanya Najeriya a ‘rukunin C’ mai kasashen Tunisiya, Uganda da Tanzania

-

 

Shugaban Nijeriya sanye da rigar Super Eagles

Tawagar kwallon kafa ta Najeriya Super Eagles ta samu kanta a rukunin C bayan raba jadawali na rukuni a gasar Kofin nahiyar Afrika,  AFCON ta 2025 da za a yi a kasar Morocco.

Daga cikin abokanan karawar ta Super Eagles a rukunin akwai kasar Tunisia sai Uganda da Tanzania.

Kasashen da ke rukunin A sun kunshi Morocco mai masaukin baki sai Mali da Zambia kana Tsibirin Comoros.

Daga rukunin B kasashen Masar wato Egypt da Afirka ta Kudu sai Angola da Zimbabwe ne za su kece raini.

Rukunin D akwai kasar Senegal da Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango  sai Jamhuriyar Benin da Botswana.

Rukunin E na dauke da kasashen Algeria da Burkina Faso sai Equatorial Guinea da Sudan. Sai rukunin karshe na F mai kasashen Cote d’Ivoire kana Cameroun da Gabon tare da Mozambique.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara