DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba a hango Atiku Abubakar ba a taron jam’iyyar PDP na yankin Arewa maso Gabas da ya gudana a Bauchi ba

-

Babbar jam’iyyar adawa ta Nijeriya PDP a yankin Arewa masu gabas ta gudanar ta taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da ya gudana a jihar Bauchi.

Taron dai ya samu halartar dukkanin gwamnonin ta uku da suka hada da gwamnan jihar Bauchi Bala Mohammed da na jihar Taraba Dr Agbu Kefas da kuma Ahmad Umar Fintiri na jihar Adamawa.

Haka kuma taron ya samu halartar Sanatoci da ‘yan majalissun wakilai da kuma ‘yan majalisar jiha daga shiyyar.

Sai dai rahotanni sun bayyana cewa tsohun shugaban kasar Atiku Abubakar bai samu halartar taron ba ko aike wa da wakili a wajen taron.

Wannan dai a iya cewa ko bai rasa nasaba da rikicin cikin gida da jam’iyyar ta PDP ke fama da shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara