DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Muna neman kari a kasafin kudi don samar da ayyukan yi – Ministan kwadago da samar da ayyukan yi Muhammad Dingyadi

-

 

Ministan kwadago Muhammad Dingyadi

Ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Muhammad Dingyadi, ya ce ma’aikatar na bukatar karin kudade cikin kasafin kudin 2025, domin bunkasa ayyukan ta.

Ya ce za a yi amfani da kudaden musamman wajen gyarawa, sake ginawa da kuma samar da kayan aiki ga cibiyoyin bunkasa sana’o’i da ke karkashin ma’aikatar da hukumomi a fadin kasar, da nufin samar da ayyukan yi ga al’umma.

Dingyadi ya bayyana haka ne a lokacin da yake kare kasafin kudin 2025, a gaban kwamitin majalisun dokoki da na dattawa. Ya ce jimillar kasafin naira biliyan 46 da aka ware wa ma’aikatar a wannan shekarar ba zai wadatar ba wajen cimma manufofin da ake so a cimma.

Dangyadi ya jaddada cewa samar da ayyukan yi ta hanyar bunkasa fasahar zamani na da matukar muhimmanci wajen cimma wani bangare na manufofin gwamnatin shugaba Tinubu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna kokarin bunkasa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan 1 – Kashim Shettima

Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya ce gwamnatin kasar na kan hanyar bunkasa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan 1 cikin shekaru goma masu zuwa. Kashim...

Yan sanda sun dakile yunkurin garkuwa da direba da fasinjoji a Katsina

Jami’an rundunar ‘yan sandan Nijeriya sun dakile wani yunkurin yin garkuwa da mutane a hanyar Funtua zuwa Gusau a Katsina. Jami’an sun yi artabu da ‘yan...

Mafi Shahara