DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaban Bola Tinubu ya nada Abba Aliyu a matsayin shugaban hukumar samar da lantarki a karkara

-

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Abba Abubakar Aliyu a matsayin babban Manajan Darakta na Hukumar bunkasa wutar lantarki a yankunan karkara (REA).
 
Wata sanarwa da Bayo Onanuga mai taimaka wa shugaban kan yada labarai ya fitar, ta ce nadin ya fara aiki daga 23 ga watan Junairu 2025.
 
Abba Abubakar Aliyu ya rike da mukamin mukaddashin manajan daraktan hukumar tun watan Maris na 2024 har zuwa lokacin da aka nada shi.
 
A baya, ya rike mukamin shugaban sashin kula da ayyuka na shirin samar da wutar lantarki ta Najeriya
Shugaba Tinubu ya yi ammanar cewa, Abba Aliyu zai yi amfani da dimbin ƙwarewar da yake da ita  don kara kawo  cigaba a hukumar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara