DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Alawar yara mai sanya maye ta fara bazuwa a sassan Nijeriya in ji hukumar NDLEA mai yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi

-

 

NDLEA

Jami’in hulda da jama’a na hukumar, ASN Sadiq Muhammad Maigatari, ya bayyana hakan a wata hira da yayi da manema labarai a Kano, ya ce wayar da kan iyaye ya zama wajibi su duba irin alewar ake kaiwa unguwanninsu.

Ya ce an kama alewar “Choculate” amma a cikinta ana zargin an lullube ta da abubuwan da ke sanya maye.

Maigatari ya ce ana zargin ana sayar da alewa a unguwanni ga yaran da ba su sani ba, a lokacin da za su je makaranta, ya kuma bukaci iyaye da su rika lura da wasu dabi’u da ‘ya’yansu ke nunawa a unguwanni da cikin gidajen su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara