DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hon. Nasir Aminu Bala Ja’oji ya dauki nauyin ‘yan karamar hukumar Tarauni 20 zuwa kasashen waje domin karo karatu

-

 

Hon. Nasir ja’oji

 A wani yunkuri na bunkasa ilimi a karamar hukumar Taruni,Hwanarabil Nasir Aminu Bala Ja’oji ya bayar da tallafin karatu zuwa kasashen waje ga ‘yan asalin karamar hukumar Tarauni guda 20 da suka cancanta a jihar Kano.

Shirin wanda kungiyar Ja’oji Organisation ke jagoranta, zai baiwa wadanda suka ci gajiyar tallafin damar samun digiri na biyu a kasashen ketare, tare da basu ilimi da kwarewa da gogewa.

Da yake jawabi a wajen Hon. Ja’oji, wanda memba ne a majalisar gudanarwa ta Kwalejin Ilimi ta Tarayya da ke Potiskum, ya jaddada muhimmancin ilimi wajen ci gaban kasa, inda ya bayyana cewa tallafawa matasa zai taimaka wajen gina rayuwar su tare da samun kwararrun ma’aikata a Nijeriya.

Ya bayyana cewa shirin bayar da tallafin karatun na da nufin samarda damammaki ga matasan Nijeriya,don suyi fice a duniya, da inganta rayuwarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara