DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin ka an yi rashawa da cin hanci da fama da matsalolin tsaro -jigo a APC ya mayarwa Buhari martani

-

 

Muhammadu Buhari

Wani jigo a jam’iyyar APC Josef Onoh, ya ce shekaru takwas da tsohon shugaba Muhammadu Buhari ya yi a kan karagar mulki na tattare da cin hanci da rashawa da kuma rashin tsaro.

Onoh ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a yayin da yake mayar da martani ga Buhari na cewa Nijeriya ta samu ci gaba sosai a harkokin tsaro da tattalin arziki a lokacin mulkinsa.

Tsohon shugaban kasar ya bayyana cewa lokacin da ya  karbi mulki tattalin arzikin Nijeriya ya rushe tare da matsalar tsaro a hannun jam’iyyar PDP da ta shafe shekaru 16 tana mulki.

Buhari, ya tabbatar da cewa a dabarun gwamnatinsa sun yi nasarar magance wadannan matsaloli, tare da dakile ayyukan ta’addanci da matsalolin tattalin arziki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara