HomeLabaraiHukumar tace finafinai ta jihar Kano ta dakatar da daukar wani fim...

Hukumar tace finafinai ta jihar Kano ta dakatar da daukar wani fim mai suna “Zarmalulu”

-

 

Hukumar tace fina-finai ta jihar Kano ta dakatar da wani film mai suna ‘Zarmalulu’ tare da gayyatar dukkannin wadanda suka fito a cikinsa domin jin ba’asi, biyo bayan zargin yin amfani da kalmar badala a matsayin sunan film din.
Hukumar karkashin jagorancin Alhaji Abba El-Mustapha ta ce ta karbi korafi daga wasu yan kishin jihar Kano akan wannan film din bisa zargin rashin ma’ana.
Abba El-Mustapha ya bayyana damuwarsa akan lamurin tare da bayar da umarnin dakatar da film din, haka kuma ya gayyaci dukkannin wadanda ke da ruwa da tsaki a shirin.
A cikin wata sanarwa daga jami’in hulda da jama’a na hukumar Abdullahi Sani Sulaiman da ya aike wa DCL Hausa, ta ce hukumar na da hurumin dakatar da dukkanin wani fim da ba ta gamsu da yadda aka shirya shi ba, tare da ladabtar da duk wanda ta samu da yin abin da bai kamata ba a cikin kowane fim.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img