Wani dan Majalisar wakilan Nijeriya daga PDP ya sauya sheka zuwa jam’iyyar APC

-

 

Majalisar wakilan Nijeriya

Dan majalisar mai wakiltar mazabar Jaba/Zango Kataf a jihar Kaduna, Amos Magaji, ya shirya sauya sheka ne bisa rikicin da ya dabaibaye babbar jam’iyyar PDP mai adawa a Nijeriya.

Kakakin majalisar Tajudeen Abbas wanda ya jagoranci zaman majalisar a ranar Talata ya karanta wasikar sauya shekar Magaji a zauren majalisar.

Magaji ya ce rikicin da haryanzu ba a warware a PDP ba tun daga matakin kasa har zuwa jiha ya sa ba zai iya zama a cikin jam’iyyar ba.

Magaji dai shi ne dan jam’iyyar PDP na uku da ya koma APC tun bayan kaddamar da majalisar ta 10 bayan Chris Nkwonta da Eriatheke Ibori-Suenu, daga jihohin Abia da Delta.

Da yake nuna adawa da sauya shekar, shugaban marasa rinjaye, Kingsley Chinda, ya bukaci kakakin majalisar da ya ayyana kujerar dan majalisar na Kaduna a matsayin wadda babu kowa kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara