DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Na yi nadamar yi wa Tinubu yakin neman zabe a 2023 – Dan Bilki Kwamanda

-

Abdulmajid Dan Bilki Kwamanda

Dan siyasa kuma jigo a jam’iyyar APC, Abdulmajid Dan Bilki kwamandan ya bayyana cewa ya yi nadamar yakin neman zaben shugaban kasa Ahmed Bola Tinubu a zaben 2023.

Dan Bilki Kamanda ya bayyana haka ne a yayin zantawar sa da Daily Trust ta wayar tarho, ya ce bisa la’akari da abubuwan da ke faruwa, Shugaba Tinubu ya gaza wa ‘yan Nijeriya da dama da suka zabe shi a 2023. 

Ya bayyana cewa a duk a rayuwarsa bai taba nadamar wani mataki da ya dauka ba kamar yadda yake nadamar yakin neman zaben Shugaba Tinubu. 

A cewar sa duk da dan jam’iyyar APC ne, amma dole ya yarda cewa gwamnatin Nijeriya karkashin jam’iyyar APC ta gaza, kuma a matsayinsa na wanda ya sadaukar da lokacinsa da dukiyarsa wajen jawo hankalin mutane su zabi jam’iyyar, yana nadamar wannan abu da ya yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara